Hausa
Sorah Ash-Shams ( The Sun )

Verses Number 15

وَالشَّمْسِ وَضُحَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 1
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
وَالْقَمَرِ إِذَا تَلاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 2
Kuma da wata idan ya bi ta.
وَالنَّهَارِ إِذَا جَلاَّهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 3
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 4
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
وَالسَّمَاء وَمَا بَنَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 5
Da sama da abin da ya gina ta.
وَالأَرْضِ وَمَا طَحَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 6
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
وَنَفْسٍ وَمَا سَوَّاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 7
Da rai da abin da ya daidaita shi.
فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 8
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.
قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 9
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.
وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 10
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 11
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
إِذِ انبَعَثَ أَشْقَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 12
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ اللَّهِ نَاقَةَ اللَّهِ وَسُقْيَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 13
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنبِهِمْ فَسَوَّاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 14
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
وَلا يَخَافُ عُقْبَاهَاSorah Ash-Shams ( The Sun ) Verse Number 15
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).